IQNA

An Buga Kur'ani Rubutun Hannu A Mauritania

22:37 - February 23, 2018
Lambar Labari: 3482421
Bangaren kasa da kasa, an buga wani kur'ani rubutun hannu da aka kira da kur'anin kasa a kasar Mauritania.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na alakhbar.info cewa, an buga kur'anin mauritaniya da aka rubuta da hannu bisa kira'ar Warsh daga Nafiu, wanda shugaban kasar ya karba a shekara ta 2011.

A cikin shekara ta 2012 shugaba Muhammad Wuld bin Abdulaziz ya kaddamar da wannan kwafin kur'ani a wurin buda bakia  cikin watan azumin Ramadan.

A halin yanzu an buga wannan kur'ani, kuma za  ayada shi a tsakanin al'ummar kasar, wanda ake kiransa da kur'anin kasa, wanda gwamnatin kasar ta kaddamar da shia  hukumance bisa kira'ar warsh wadda ake yi a kasar.

Ma'aikatar kula da harkokin addini takasar ce ta dauki nauyin dukkanin ayyukan buga kur'anin da kuma rarraba shi.

3693833

 

captcha