Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin Alkafil cewa, kamar kowace shekara a kasar Iraki an dora tutocin makokin shahadar Imam Hussain (AS) a hubbarorin limaman shiriya na iyalan gidan manzo (SAW) a lokacin da ake shirin fara tarukan ashura.
An fara gudanar da wannan aiki ne tun a daren jiya Litinin, da hakan ya hada da hubbaren Imam Hussain (AS) da kuma hubbaren Abbas (AS) da suke a birnin Karbala.
Sai kuma a birnin Najaf an dora wadannan tutocia kan hubbaren Imam Amirul Mumimin (AS).
Masu jawabi kan waki’ar Karbala za su fara gudanar da jawabansu a wadannan wurare masu alfarma a cikin wadannan kwanaki na watan muharram.