Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, a lokacin da tawagar Iran karkashin jagoran Ainullah Qashqawi da kuma Hassan Ismati zuwa yankin Tuba birnin 'yan darikar Muridiyyah, Qashqawi ya bayyana cewa, kasantuwar mabiya darika mutane ne masu son addini da son manzon Allah da ahlul bait, ko shakka babu suna babbar gudunmawa da za su bayar wajen hada kan al'ummar musulmi.
Bayan na kuma sun ziyarci garin Kaulak na mabiya darikar Tijaniyya, inda a can ma suka gan ada Sheikh Ahmad Tijani Nyas shugaban darikar Tijaniyyah masu bin tafarkin faila.
Tattaunawar bangarorin biyu ta mayar da hankali ne kan wajabcin karfafa hadin kan al'ummar musulmi da kuma bin hanyoyi na ilimi domin wayar da kai kan hakiaknin musuluncin manzon Allah, wanda ya koyar da zaman lafiya a tsakanin al'ummomi.